Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Za a samar da kotun tafi da gidanka kan Coronavirus a Jigawa

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa tace zata samar da kotun tafi da gidanka domin hukunta masu take dokar kulle da zaman gida da gwamnatin ta sanya a wasu sassa na jihar da aka samu bullar cutar Corona.

Gwamnan jihar Muhammad Badaru Abubakar ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin Talatar nan a fadar gwamnatin jihar.

Wakilin Freedom Radio a Jigawa Aminu Umar Shuwajo ya rawaito mana cewa gwamna Badaru ya nuna takaicinsa kan rahotonnin da ake samu na yadda wasu al’umma ke yin ka rantsaye ga dokar.

Haka kuma gwamnan ya kara da cewa duk mutanen dake son a bude garin su daga wannan doka ta zaman gida, to ya zama tilas sai an gamsu da yadda suke bin dokar sau da kafa kafin fatan su ya cika.

Labarai masu alaka:

Covid-19: Gwamnatin Jigawa ya amince a gabatar da sallar idi

Za a tsaurara dokar kulle a Jigawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!