Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a samar da kotuna na musamman kan hukunta masu cin zarafi – Buhari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta fara aikin samar da Kotuna na musamman da za su hukunta masu aikata laifukan da suka shafi cin zarafin jama’a musamman fyade da makamantansu.

Ministan sjari’a kuma Atoni Janar na tarayya Abubakar Malami ne ya tabbatar da hakan yayin taro na musamman da aka gudanar da kafar intanet, kan al’amuran da suka shafi cin zarafi da kuma ayyukan ta’addanci.

Sashen yaki da miyagun kwayoyi da muggan ayyuka na majalisar dinkin duniya ne, a wani bangare na bikin ranar mata da duniya ta bana, wanda ake gudanar da taron kasa da kasa a birnin Kyoto na Japan.

Malami ya yi karatun baya kan wani kwamitin yaki da ayyukan fyade da cin zarafi da ya kafa a bara, wanda yake aiki a karkashin ministocin kasar nan.

Haka zalika Abubakar Malami ya shaida cewa gwamnatin tarayya tana iya kokarinta na ganin ta kawo karshen ayyukan ta’addanci da sace-sacen mutane don garkuwa da su a kasar nan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!