Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Za ayi zubeben kwarya tsakanin malaman Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce nan bada jimawa da zarar wucewar annobar Covid-19 za ta shirya wata gagarumar Mukabala a tsakanin bangarorin addini dake jihar, domin kawo karshen gutsiri-tsoma dake faruwa a tsakanin su.
Kwamishinan al’amuran addini na jihar Kano, Malam Muhammad Tahar Baba Impossible shi ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da wakilin mu Yusuf Ali Abdallah a yau Laraba.
Baba Impossible yace, biyo bayan takun saka da ake yawan samu kan batanci ga addini tare da wuce gona da iri daga wasu al’umma, ya sanya daukar wannan mataki domin rarrabewa da baccin makaho.
Har ila yau, Impossible ya ce, a kwanakin baya jami’an tsaron farin kaya DSS sun gayyaci dukkan bangarorin malaman addini dake jihar, inda ta gargadesu kan su ja kunnen mabiyansu wajen kaucewa daukar doka a hannu.

Karin labarai:

Baba Impossible ya musanta fatawar da Maigida Kacako ya bayar

Kowa yazo ya dauki dan sa daga makarantun Mari ko mu dauki mataki –Gwamnatin Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!