Connect with us

Labarai

Za mu gyara manyan asibitocin 21- Gwamnatin Sokoto

Published

on

Gwamnatin jihar Sakoto, ta ce, za ta gyara manyan asibitocin jihar guda 21 domin ganin tsarinsu ya yi dai-dai da na zamani.

 

Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Faruk Abubakar, ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

 

Ya kuma ce, gwamnatin ta ware miliyoyin kudade da aikin zai cinye, wanda idan aka fara ba za a tsaya ba har sai an kammala ayyukan.

 

Dakta Faruk Umar Abubakar ya ce, a halin yanzu gwamnati ta fara aikin gyara cibiyoyin lafiya guda 125 da ake da su a jihar.

 

Haka kuma, ya kara da cewa, an yi hakan ne domin saukaka wa mutanen da ke yankunan Karkara na tururuwar da suke yi zuwa asibitocin da ke cikin garuruwan jihar ta Sokoto.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!