Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu kawo karshen siyasar jagaliya a Kano – Kwamishinan ‘yan sanda

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce za ta yiwa siyasar jihar Kano garanbawul domin magance rikice rikicen ‘yan jagaliyar siyasa na sare sare.

 

Kwamishin ‘yan sandan Kano Samaila Shuaibu ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai

 

Samaila Shuaibu ya ce hakan ba zai samu ba har sai an samu hadin kan malaman addinai da sauran masu rike da masarautun gargajiya har ma da gwamnatin Kano don tabbatar da tsaro a jihar baki daya.

 

Samaila Shuaibu ya ce, matukar ‘yan jaridu da sauran kungiyoyin kare hakkin al’umma da na matasa yan kishin kasa suka bada hadin kai ga rundunar ‘yan sandan shakka babu za’a samu raguwar aikata muggan laifuka a Kano.

 

Samaila Shuaibu ya kuma ce za a tabbatar da tsaro ga duk wanda ya kai wa rundunar bayanan sirri don bankado maboyar batagari da sauran guraren masu aikata laifuka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!