Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu kwato sama da miliyan 588 da aka biya likitoci ba bisa ƙa’ida ba – Chris Ngige

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce ta gano kudi naira miliyan 588 da aka biya wasu likitoci ba bisa ka’ida ba, kuma da sannu za ta kwato su.

Ministan kwadago da samar da aikin yi Dr Chris Ngige ne ya tabbatar da hakan ga manema labaran fadar shugaban kasa, inda ya ce an biya kudaden ne ga likitoci masu neman kwarewa bisa kuskure, maimakon wasu likitocin.

Dr Ngige ya ce sun gano sunayen ne bayan bincike da suka gudanar a kan likitoci dubu takwas da shugaban cibiyoyin lafiya na tarayya suka mikawa gwamnati domin wani horo da za a yi musu.

To sai dai ya ce wasu likitocin sun mayar da kudin, yayin da kuma ake shirin karbo sauran.

Game da yajin aikin da likitocin suke yi kuwa, ministan ya ce gwamnatin tarayya tana nan a kan bakanta na kin biyan likitocin da ba sa zuwa aiki, domin tsarin a a cikin dokokin kwadago na duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!