Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Likitoci za su shiga yajin aiki a Legas

Published

on

Kungiyar likitoci ta Jihar Lagos ta ce daga gobe litinin za ta fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku, bayan da gwamnatin jihar ta gaza cika ma ta alkawuran da ta dauka na biya mata wasu bukatunta.

Shugaban kungiyar Dr. Oluwajimi Sodipo ne ya sanar da hakan yayin taron manema labarai ranar Lahadi a Lagos, bayan karewar wa’adin da suka baiwa gwamnatin.

Dr Oluwajimi Sodipo ya ce tun a ranar 27 ga watan Yunin da ya gabata ne suka cimma matsayar karawa gwamnatin wa’adin makonni biyu domin biya musu bukatunsu akalla kashi 70 cikin 100, bayan karewar na kwana 21 da suka bayar tun farko, wanda kuma hakan ba ta samu ba.

Karin labarai:

Legas ta koka kan yawan samun masu Corona a jihar a kullum

Wani gini mai hawa uku ya ruso a Legas

Daga cikin bukatun na su akwai neman dai-daita albashinsu da na likitocin da ke aiki karkashin gwamnatin tarayya, da biyan bashin albashin watanni biyu da likitocin da ke cibiyoyin killace masu fama da cutar Covid-19 a Jihar ke bin gwamnatin.

Sai kuma batun karancin likitocin da ake fama da shi a Jihar, wanda kungiyar ta bukaci a kawo karshen matsalar, da kuma bunkasa walwalar likitocin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!