Connect with us

ilimi

Za mu magance duk matsalolin da Dawakin Kudu ke fuskanta- Mai Rago

Published

on

Majalisar Karamar hukumar Dawakin Kudu, ta ce za ta ci gaba da shiga lungu da Sako na yankunan da ke karkashinta domin  magance duk wasu matsaloli da al’ummar yankunan ke fuskanta.

 

Shugaban karamar hukumar Alhaji Sani Ahmad Mai Rago, ne ya bayyana hakan, yayin wata ziyara da al’ummar garin Dabar Kwari suka kai masa a ofishinsa.

 

Alhaji Sani Ahmad Mai rago ya Kara da cewa babban aikin da karamar hukumar ta Sanya a gaba, sun hada da gyara makarantun yankin da Kuma inganta fannin koyo da koyarwa.

 

Shugaban karamar hukumar ta Dawakin Kudu Alhaji Sani Ahmad Mai rago ya Kuma bukaci hadin kan al’ummar yankin, domin ci gaba da amfanar abubuwan more rayuwa.

 

A nasa jawabin Alhaji Danladi Luran, a madadin mutanen na Dabar Kwari, ya bayyana cewa yankin na su na fama da matsalar rashin makarantar Islamiyya, don haka ya bukaci shugaban karamar hukumar da ya samar musu da makarantar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!