Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Za’a magance matsalar titi a Tarauni- Hafiz Kawu

Published

on

Korafin da al’ummar mazabun unguwa UKU cikin gari da kauyen Alu ke yi na rashin kyawun titin da ya tashi daga Tsamiyar mashaya zuwa tashar unguwa uku, ya fara zama tarihi biyo bayan fara aikin titin da dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Tarauni Hafiz KAWU ya bayar.

Mazauna yankunan dai sun ce rashin kyawun hanyar ta janyo musu shiga halin tasku tsawon lokaci da dama.

“Hajiya Halima Muhammed Limawa daya ne daga cikin iyaye mata da ke mua’amala a titin da ya tashi daga tsamiyar mashaya a kullu yaumin, ta shaiwada freedom rediyo cewa suna shiga mawuyacin halin a duk lokacin damina sanadiyar rashin kyawun titin”.

 ‘‘Titin wanda tun farko aka samar dashi kusan shekaru ashirin da suka gabata, ya bukaci gyara amma gwamnati-bayan gwamnati sun zo ba tare da samun nasarar magance shi ba’’, a cewar Hajiya Limawa.

A yayin wata ziyarar da tashar Freedom rediyo ta kai wajen da ake gudanar da aikin, wasu daga cikin al’ummar yankunan sun ce gyara musu titin a wannan lokaci, zai dauke musu daya daga cikin manyan kalubale da ke addabarsu.

Yadda al’ummar Dawakin Kudu suka koka kan matsalar hanya

An daidaita tsakanin KAROTA da ‘yan kasuwa bayan dakatar da tsayawar Tireloli akan titi

“Sun ce a sau da yawa, sun sha kaiwan korafi kan titin ga hukumomi amma ba a daukar mataki, shi yasa wannan karon su ke fata ganin an kammala aikin kamar yadda ya kamata”.

Alhaji Hassan Yahaya Kila shine wanda ya wakilci dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Tarauni Alhaji Hafiz Kawu wajen duba aikin, ya shaidawa manema cewa, nan ba da dadewa ba za a kammala kwaskwarima ga titin kafin daga bisani ayi mai aiki mai gaba daya.

Ina tabbatar da muku tuni an sa aikin cikin ayyukan mazabu na dan majalisar tarayyar ta Tarauni kuma nan ba dadewa ba za’a fara aikin gadan-gadan shi yasa muka fara yin kwaskwarima don ragewa al’umma wahalhalun da suke fuskanta a wannan lokaci na damina”.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!