Labarai
Za mu rika bibiyar ayyukan Malamai da makarantu- SUBEB

Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Kano SUBEB ta ce, za ta rinka bibiyar ayyukan Malamai da makarantu dan ganin yadda ake gudanar da koyo da koyarwarwa a makarantun Kano a wani bangare na inganta ilimi.
Hakan na cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na ma’aikatar ta SUBEB Balarabe Danlami Jazuli ya fitar.
Sanarwar ta ce kwamishina na Ɗaya a hukumar, Alhaji Wada Ibrahim Daho, ne ya bayyana hakan a lokacin da ya jagoranci tawagar manyan jami’an hukumar zuwa Ƙaramar Hukumar Rimin Gado domin duba yadda harkokin koyarwa da koyo ke gudana a makarantun yankin.
Da yake yi wa jami’an sashen ilimi na ƙaramar hukumar bayanin sakamakon ziyarar, Alhaji Wada Ibrahim Daho ya ce manufar tura manyan jami’an na SUBEB zuwa ƙaramar hukuma guda a lokaci guda ita ce gano matsalolin da ke kawo cikas ga ci gaban ilimi tare da samar da hanyoyin magance su.
Ya ƙara da cewa ayarin ya tantance yadda harkokin koyarwa da koyo ke gudana a makarantun yankin, inda ya yaba wa malamai da shugabannin Karamar Makarantar Sakandiren Gulu bisa yadda suke gudanar da ayyukansu.
Sai dai ya nuna damuwa kan yadda wasu malamai a Makarantar Firamaren garin na Gulu ke yawan makara zuwa aiki duk da kasancewarsu ‘yan asalin garin.
You must be logged in to post a comment Login