Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu samar da asusun bunkasa ayyukan Noma a Najeriya – Majalisar dattijai

Published

on

Majalisar dattijai ta amince da kafa asusun bunkasa ayyukan Noma na kasa da nufin samar da kudi don tallafawa dabarun bunkasa harkokin noma a Najeriya.

Wannan dai ya biyo bayan gabatar da rahoto da kwamitin majalisar dattijai kan harkokin Noma da raya karkara yayi a zaman majalisar na ranar Laraba 24 ga watan Maris 2021.

Shugaban kwamitin Sanata Abdullahi Adamu ne ya gabatar da rahoton tun da farko, inda ya bukaci a sake karanta kudirin a karo na biyu, wanda ya samu karatu na farko tun a ranar 4 ga Maris na shekarar 2020.

A cewarsa, kudirin na neman bunkasa ayyaukan noma tare da samar da kudade domin tallafawa bangaren a kasar nan, domin tabbatar da samar da abinci da wadatarsa a Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!