Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje ya kaddamar da kwamitin kula da ayyukan Burtalai

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da babban kwamitin da zai rika kula da harkokin Burtalai a nan Kano.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya kaddamar da kwamitin ne a yau wanda manajan daraktan hukumar bunkasa aikin noma da raya karkara na jihar Kano Ibrahim Sulaiman Dan’isle zai jagoranta ta wanda aka kaddamar a ofishin su.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Kuma kaddamar da rabon motoci da babura wanda yace gwamnati da masu taimaka mata sun samar da su ne ga manoma don rika amfani dasu don saukaka zirga-zirga

A yayin taron gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Kuma ce Kara da cewa dokar da shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi ta hana shigo da abinci daga waje ta taimakawa manoma wajen yin noma a kasar nan tare cin riba.

Gwamnnatin Kano ta shawarci manoma dasu kalli noma a matsayin riba

Yadda aka sami arangama tsakanin manoma da makiyaya a Jigawa

RIFAN za ta tallafawa manoman da ambaliyar ruwa ta shafa a Kano

A nasa bangaren manajan daraktan hukumar bunkasa noma da Raya karkara na Kano Ibrahim Sulaiman Dan’isle ya godewa gwamnatin Kano bisa ga samar da motoci da baburan zirga-zirga ga manoma.

Wakiliyar mu Zahrau Nasir ta ruwaito cewa kwamitin harkar Burtalin Yana da wakilici daga wasu maaikatu a nan Kano tare da kuma Masaurautun Kano biyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!