Addini
Za mu sanya kafar wando daya da masu sana’ar DJ- Hisbah

Hukumar Hisbah ta jihar kano, ta sha alwashin sanya kafar wando daya da duk masu gudanar da sana’ar DJ musamman masu yin amfani da kalaman da ba su kamata ba da kuma sanya wakokin batsa a lokacin shagalin bukukuwa.
Mataimakin Babban Kwamandan hukumar ta Hisbah na jihar Kano, Dakta Mujahidden Aminidden, ne ya bayyana hakan a wata zantawarsa da Wakilinmu Abba Isah Yakasai.
Dakta Mujahiddin Aminudden ya kuma bayyana cewa, hukumar ba za ta lamunci aikata irin wadannan munanan dabi’u ba.
You must be logged in to post a comment Login