Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Za’a fara darusan yaki da rashawa a jami’ar ABU

Published

on

Mukaddashin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa EFCC lbrahim Magu ya ce kwalejin hukumar zata samar da kwasa-kwasai kan yadda za a dakile cin hanci da rashawa a cikin al’umma.

Ibrahim Magu ya ce wannan na daga cikin dimbin hanyoyin da hukumar ta bullo da su don yaki da cin hanci da rashawa a kasar nan.

Magu ya bayyana hakan ne yayin sanya hannu kan yarjejeniyyar fahirmtar juna da jamiar Ahmadu Bello dake Zari’a.

Da dumi-dumi: EFCC ta cafke Muntari Ishaq Yakasai

Hukumomi kadai ba za su iya magance cin hanci da rashawa ba- EFCC

Hukumar EFCC za ta fara gurfanar da Angwaye a Kotu

Yarjejeniyyar za ta sanya kwalejin hukumar yaki da cin hanci da rashawa dake Karu a babban birnin tarayya Abuja da kuma jami’ar samar da kwasa-kwasai na yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifuka.

Da yake jawabi tun da fari, shugaban jami’ar ta Ahmadu Bello Farfesa Ibrahim Garba ya ce shakka babu yarjejeniyyar tsakanin jami’ar da kwalejin zata taimaka wajen cike gibin da ake da shi wajen yaki da wannan ta’ada.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!