Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An dakatar da manyan ma’aikata 12 na hukumar EFCC

Published

on

Manyan ma’aikata 12 ne na hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC suka karbi takardar  dakatarwa a jiya Litinin

Da yawa daga cikin na rike da manyan bincike na yaki da cin hanci da rashawa da ake yi a halin yanzu.

Daya daga cikin ma’aikata da ya nemi a saka sunan sa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja cewa tun da suka fara aiki ba’a taba tuhumar su da laifi ba, amma sun rungumi kaddara kan wannan batun.

Tun farkon nadin Ibrahim Magu a matsayin mukaddashin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa EFCC wasu na ganin cewa bai can-canci rike mukamin ba, la’akari da rahoton rashin can-canta game dashi da hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta bayar tun a wancan lokacin.

Rubutu masu alaka :

Za a janye ‘yan sandan dake aiki a EFCC

Hukumar EFCC ta gano ma’aikatan bogi 1000 a jihar Kwara

EFCC: ta gargadi ‘yan Najeriya da su guji bada gudunmawar karya

Haka ma dai aka yi ta dambarwa a majalisar dattijai bayan da aka mika sunan Ibrahim Magu, inda ‘yan majalisu suka ki amincewa dashi, sai dai fadar shugaban kasa ta tsaya kai da fata akan ganin an tabbatar dashi a mukamin, wanda a yanzu kuma ake ganin sun raba hannun riga.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!