Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu ciyo bashi domin cike giɓin kasafin shekarar 2022- Ministar Ƙudi

Published

on

Gwamnatin tarayya na shirin karɓo bashin Naira tiriliyan 4 da biliyan tamanin da tara daga cikin gida da waje don cike giɓin kasafin kuɗinta na shekara 2022 da ya kai sama da Naira tiriliyan sha uku da biliyan casa’in da takwas sakamakon rashin samun kuɗaɗen shiga.

Ministar kuɗi kasafi da tsare-tsaren Hajiya Zainab Ahmad ce ta bayyana hakan a Abuja, a wani taron tattaunawa da kwamitin majalisar wakilai kan sha’anin kuɗi.

Zainab Ahmad ta ce, faɗuwar darajar naira da sauye -sauyen da babban bankin Najeriya ya yi a baya -bayan nan ya ƙara dagula harkokin samun kuɗi a Najeriya.

A cewar ta matakin matsin lamba kan kasuwar canjin kuɗaɗen waje ya taka rawa, har ma ta ce har yanzu masu zuba jari ba su dawo kasuwar hada hadar canji a Najeriya ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!