Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu hukunta masu cunkuson jama’a-FRSC

Published

on

Hukumar kiyaye abkuwar hadurra ta kasa FRSC, za ta fara kama masu cun kusa  jama’a a ababen hawa.

Hukumar kiyaye abkuwar hadurra ta kasa (FRSC), ta ce za ta fara daukan tsauraran matakai kan masu ababen hawa da ke yin lodin wuce kima.

Mai magana da yawun hukumar a nan Kano, Kabiru Ibrahim Daura ne ya bayyana haka yayin zantawa da tashar freedom rediyo.

Kabiru Ibrahim Daura, ya ce, daukar matakin ya zama wajibi domin dakile yaduwar cutar Corona wacce ta ke da saurin yaduwa a cikin al’umma ta hanayar yaduwa.

Labarai masu alaka.

Takai:Mutane 19 ne suka rasa rayukansu a wani hatsari da ya afku a kauyen Dinyar Madiga

Ganduje : za’a rufe kan iyakokin jihar Kano COVID-19

“Ko da masu baburan hawa ba a amince su dauki sama da Mutum biyu ba, ma’ana da mai tuka babur din da Kuma Mutum daya” inji Kabiru Ibrahim Daura’’.

Ya ce tun farko dama yin lodin wuce kima laifi ne, saboda haka hukumar  za ta kara sanya ido kan lamarin  domin kare lafiyar al’ummar jihar Kano dama kasa baki daya.

Wakilin mu Abdullahi Isa, ya ce hukumar ta sha alwashin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an samu takaitar zirga zirga don dakile barzanar yaduwar cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!