Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zanga-zanga ta tilasta rufe gidan talabijin din kasar Mali

Published

on

Masu zanga-zanga a Mali sun tilasta wa kafar yaɗa labaran ƙasar katse shirye-shiryenta yayin wani gagarumin jerin gwano a Bamako, babban birnin ƙasar.

‘Yan sanda sun hah-harba bindiga kuma sun yi amfani da hayaƙi mai sa hawaye don tarwatsa masu zanga-zanga a dai-dai lokacin da wasunsu ke ƙoƙarin kutsawa cikin ginin majalisar dokokin ƙasar.

Wannan ce zanga-zanga karo na uku cikin wata guda da ake gudanarwa a kasar don neman Shugaba Ibrahim Boubakar Keita ya sauka daga kan mulki.

Cikin koke-konen al’ummar kasar akwai rashin gamsuwa kan yadda ake tunkarar rikicin masu iƙirarin jihadi da ya shafe tsawon lokaci, da matsalolin tattalin arziƙi da kuma taƙaddama game da zaɓukan ‘yan majalisa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!