Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin rashawa: An fara mayar wa da malamai kuɗin addu’ar da aka zaftare musu

Published

on

Hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da rashawa ta Kano ta ce, tuni waɗanda ake zargi da zaftarewa malamai kuɗin addu’a suka fara mayar da kuɗin ga waɗanda suka karɓarwa, ta hannun hukumar bayan da ta ƙaddamar da bincike a kai.

Shugaban hukumar Muhyi Magaji Rimin Gado ya shaidawa Freedom Radio cewa, binciken su ya tabbatar da zarge-zargen da aka yiwa mai baiwa gwamnan Kano shawara kan addinai da ɗansa da kuma wasu mutane, na zaftarewa malamai kuɗin addu’ar da gwamna ya basu.

A cewar Muhyi yanzu haka sun mayarwa da mutane bakwai kuɗaɗensu sannan suna ci gaba da faɗaɗa bincike a kai tare da tattara ƙarin hujjoji domin gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.

Ya ƙara da cewa, abin da mai baiwa gwamnan shawara da waɗannan mutane suka aikata na wabcewa malaman kuɗin addu’a ya saɓa da doka, kuma a yanzu sun samu gamsassun dalilai waɗanda suka tabbatar da hakan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!