Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan sanda sun musanta yin kisan kai a Kano

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta musanta zargin cewa jami’anta sun hallaka wani matashi Saifullahi Abdullahi mai shekaru 23 a unguwar Ƙofar Mata da ke ƙaramar hukumar Birni.

Mai magana da yawun ƴan sandan Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa cikin wani saƙon murya da ya aike wa Freedom Radio ya ce, tun farko sun samu rahoton ɓarkewar fadan daba ne a unguwar Ƙofar Mata da ƙarfe 1 da mintuna 40 na dare.

Ya ce, “Ƴan sanda sun halarci wurin tare da kama mutane biyu suka sanya musu ankwa, sannan suka bar su tare da ɗan sanda guda ɗaya a mota, suka bazama cikin unguwar domin faɗaɗa bincike, sai dai kafin su dawo wasu da ake zargin ƴan daba ne suka dawo inda motar ta ke suka kuɓutar da waɗanda aka cafke, sannan suka yiwa ɗan sandan da aka bari rauni tare da wani mutum guda.”

Ƴan sanda sun garzaya da ɗan sandan da aka yiwa rauni da kuma mutum ɗaya mai suna Saifullahi Abdullahi zuwa asibiti wanda a nan ne kuma rai ya yi halinsa a cewarsa.

Ƙarin labarai

Jami’an tsaro sun gayyaci masu shirya zanga-zanga a Kano

#EndSARS : Buhari ya gargadi masu zanga-zanga

Mazauna unguwar dai sun zargi ƴan sandan da hallaka matashin inda har suka gudanar da zanga-zanga wadda ta kai ga lalata motar ƴan sanda guda ɗaya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!