Labarai
Ƴan bindiga sun yi garkuwa da dattijan ƙauye a Maradun

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da dattijan wani ƙauye a ƙaramar hukumar Maradun da ke jihar Zamfara bayan sun yi yunƙurin yin sulhu sanadiyyar rashin tsaron da ke addabar yankin.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Magamin Diddi wanda rahotanni suka ce yana a kusa da ɗaya daga cikin dazukan da ƴan fashin daji ke da sansani.
A tattaunawarsa da BBC, shugaban ƙaramar hukumar Maradun Sunusi Ahmed Dosara ya tabbatar da faruwar lamarin, in da yace daga ƙididdigar da suka yi mutanen da ƴan fashin dajin suka riƙe “sun kai 39”.
Zamfara na cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da suka daɗe suna fama da matsalar ƴanfashin daji masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.
Ayyukan ƴan bindigar sun durƙusar da harkokin tattalin arziƙi a yankin, musamman noma, wanda akasarin al’ummar yankin ke dogaro da shi.
You must be logged in to post a comment Login