Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya rantsar da Joseph Olasunkanmi a matsayin sabon Ministan Lantarki

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Joseph Olasunkanmi Tegbe a matsayin sabon Ministan Wutar Lantarki, sannan ya rantsar da Ambasada Sola Enikanolaiye a matsayin Karamin Ministan Harkokin Waje. An gudanar da bikin rantsarwar a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Litinin, tare da halartar iyalan ministocin da manyan jami’an gwamnati.

Nadin sabbin ministocin ya biyo bayan murabus din tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, da tsohon Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, domin ci gaba da harkokinsu na siyasa. Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin sabbin ministocin a ranar 6 ga Mayu, 2026.

Sabon Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe, kwararre ne a fannin tattalin arziki da gyaran cibiyoyin gwamnati, yayin da Ambasada Sola Enikanolaiye tsohon jami’in diflomasiyya ne da ya yi aiki a ma’aikatar harkokin waje na tsawon shekaru 35, tare da wakiltar Najeriya a kasashe da dama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!