Labarai
Takarar da zan yi a zaben 2027 ce ta ƙarshe a neman kujerar shugaban ƙasa- Atiku

Madugun adawar siyasar Najeriya Alhaji Atuku Abubakar ya ce, takarar da zai yi a kakar zabe ta 2027 ce za ta zama ta ƙarshe da zai yi domin neman kujerar shugabancin ƙasar nan.
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya bayyana hakan kwana biyu bayan babban taron da jam’iyyar su ta ADC ta gudanar a babban birnin tarayya Abuja.
Atiku dai na daga cikin jiga-jigan jam’iyyar haɗaka ta ADC da ake sa ran su fafata wajen neman tikitin jam’iyyar a zaɓen fidda gwani domin tunkarar shugaba Bola Tinubu a zaɓe mai zuwa na shekarar 2027.
You must be logged in to post a comment Login