Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaba Buhari ya kaddamar da sabbin jiragen shalkwabta guda 2

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yaki da ‘yan ta’adda da dakarun kasar nan ke yi a wannan lokaci, yana haifar da ‘Da’ mai ido.

Shugaba Buhari ya ce sojoji ba ko shakka cikin shekara hudu da suka gabata, sojojin kasar nan suna aiki tukuru domin dakile matsalolin tsaro a Najeriya.

Shugaban kasar wanda mataimakin sa farfesa Yemi Osinbajo ya wakilta ya bayyana hakan ne a dandalin Eagles Square da ke Abuja, yayin wani bikin cika shekaru hamsin da biyar da kafa rundunar sojojin sama na kasar nan.

A yayin taron shugaban kasar ya kuma kaddamar da wasu sabbin jiragen shalkwabta guda biyu da rundunar sojin saman kasar nan ta saya abaya-bayan nan.

Da ya ke gabatar da nashi jawabi, babban hafsan sojin sama na kasar nan Air Marshal Sadique Abubakar, ya ce, rundunar za ta ci gaba da kokari don dakile ayyukan batagari.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!