Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kama masu garkuwa da mutane 93

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce, takama masu satar mutane suna garkuwa da su a yankin arewacin Najeriya guda 93.

Mai magana da yawun rundunar DCP Frank Mba ne ya bayyana haka lokacin da ya ke holin batagarin a kauyen Katari da ke kan titin Kaduna zuwa Abuja.

Ya ce jami’an Operation Puff Adder ne suka samu nasarar kama mutanen cikin makwanni biyu da suka gabata.

A cewar sa, sun samu nasarar kama ‘yan ta’addar ne sakamakon bullo da sabbin dabarun dakile ayyukan batagarin.

DCP Frank Mba ya kuma ce masu satar mutanen suna garkuwa da su an kama su ne a sassa daban-daban na arewa ; kuma an kamasu da bindigogi kirar AK47 guda 35 da AK47 kirar gargajiya guda goma da alburusai guda dari biyar da kuma na’urar harba roka guda daya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!