Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar ‘yan sanda ta Kano zata fadada bincike a Anambra

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce, za ta yi duk me yiwuwa wajen ganin ta ceto sauran yaran nan talatin da takwas wadanda ake zargin wasu mutane sun sace sun kai su jihar Anambra.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Kano DSP Abdullahi Haruna kKiyawa ne ya bayyana hakan ta cikin shirin duniyar mu a yau, na nan tashar freedom rediyo da ya mai da hankali kan batun ceto wasu yara tara ‘yan asalin jihar Kano a jihar Anambra.

Ya ce, tun bayan samun nasaran ceto yaran, suka fadada binciken su domin gano ragowar.

Kungiyar iyayen yara: ‘ya’ya 47 aka sace mana

Iyayen yaran da aka sace sun bukaci taimakon al’umma

Kano: Yan sanda sun kama wani da ake zargin dan Boko Haram

Daya daga cikin iyayen yaran da aka ceto su, ya shiga tsaka mai wuya lokacin da aka sace ‘yar sa mai suna ‘Amira’ sannan aka sauya mata suna Chinyere yace ya kado matuka da samun wannan labarin

Sakataren kungiyar iyayen yara da suka batan Malam Shuaibu Ibrahim Attajiri cewa ya yi, kungiyar tana iya kokarinta wajen ganin an ceto sauran yaran, nan bada jimawa

A nasa bangaren Malam Ibrahim Khalil kokawa ya yi game da rashin bai wa bangaren tsaro mahimmanci a cewar sa, hakan ya bada gudunmawa wajen faruwar lamarin.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!