Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Cin zarafin mata ya yi yawa a Kano –Farfesa Hadiza Galadanci

Published

on

Kungiyar tallafawa mata da sana’o’in dogaro da kai wato Women’s Organization for Relief and Empowerment, (WORE) wadda mai dakin sarkin Kano Mallam Muhammadu Sanusi II, Hajiya Maryam Muhammadu Sanusi II take jagoranta, ta gabatar da wani taro mai taken “Rikicin dake faruwa tsakanin iyali, da hanyoyin da za’a magance su”
A yayin taron an tattauna matsalolin da ‘ya’ya mata ke shiga a gidajen Aurensu wanda sanadiyar hakan yakan sanya su shiga harkar shaye-shaye, da ciwon damuwa.
Farfesa Hadiza Galadanci na daya daga cikin wadanda suka gabatar da makala a wajen taron, ta bayyana cewa a matsayinta na likita tana karbar matsalolin cin zarafi na cikin gida babu adadi, wadanda suka hadar da duka,mari, da sauran su.
Wakiliyar mu Samira Sa’ad Zakirai ta rawaito mana cewa,taron ya samu halartar manyan mata daga sassa daban-daban na kasar nan wadanda suka hadar da Farfesa Rukayya El-rufa’I, da Sanata Baraka Sani, da Malama Halima Shitu, da mai dakin gwamnan jihar Sakoto Hajiya Mairo Maryam Aminu Waziri Tambuwal, da kuma wakiliyar (Yaya Susan to Plss need it)mai dakin gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-rufa’I, sai Dakta Hauwa Abdullahi, da Farfesa Aisha Tofa, da Maryam Ahmad Sabo MNI, da kuma Malama Ummukulsum Kassim.

Rubutu masu alaka:

Maza sunfi bada muhimmanci ga sunnar karin aure –Halima Shitu

Tilas a magance cin zarafin mata- Mai dakin Sarkin Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!