Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Masu fama da cutar koda sun roki gwamnati ta mayar da wankin Koda kyauta

Published

on

Masu fama da cutar Koda a jihar Kano sun roki gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje kan ya mayar da yin aikin wankin koda kyauta a jihar.

Jihar Kano dai ita ce jihar da ta kere sauran jihohi yawan masu fama da cutar koda a Najeriya, a don haka masu fama da larurar suka garzayo shirin Inda Ranka na nan Freedom Radio, inda suka nemi gwamnatin jihar tayi duba na tsanake domin kulawa da lafiyar su.

A cewar su tuni Gwamnan jihar Borno Farfesa Baba Gana Zulum ya mayar da aikin wankin kodar kyauta a jihar sa, a don haka jihar Kano ita tafi can-canta da tayi wannan aiki.

A karshe masu cutar sun bayyana yadda suke kashe kudade a kowane lokaci don wannan jiyyar.

Labarai masu alaka:

Gwamnatin Kano za ta fara karrama ma’aikatan lafiya

Abubuwan da ya kamata ku sani gami da lafiyar Idanu

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!