Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Akwai bukakatar samar da tsarin bada lafiya mai nagarta ga marasa lafiya-hukumar asibitoci

Published

on

Hukumar gudanarwar Asibitocin jihar Kano ta bukaci Asibitocin gwamnatin jiha da su samar da tsarin bada lafiya mai nagarta ga marasa lafiyan fadin jihar Kano.

Shugaban hukumar Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi, yayin taron watannin ukun karshen shekara, domin tattaunawa kan batutuwan da suka faru a bangaren lafiya a baya.

Shugaban hukumar, wanda ya samu wakilcin daraktan sashen lura da aikin likitanci na hukumar Dakta Muhammad Dahiru Shehu, ya ce ya lura da cewa akwai bukatar inganta tsarin kula da marasa lafiya a Asibitocin jihar Kano baki daya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!