Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

A kullum muna ciyar da mutane dubu 75 abincin buda baki a Kano – Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, tun bayan fara azumin watan Ramadan, a duk rana tana ciyar da mutane dubu 75 da abincin buda baki a kananan hukumomi 8 da ke cikin birnin Kano.

Mai taimakawa gwamnan Kano na musamman kan kafofin yada labarai na radio da talabijin, Abubakar Kofar-Naisa ne ya bayyana haka ga manema labarai.

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannunsa, da ya rabawa manema labarai, ta ce, akwai cibiyoyin rabon abinci akalla guda dari da hamsin a kananan hukumomi takwas da ke birnin Kano.

Abubakar Kofar Na’isa wanda shine jami’in yada labaran kwamitin kula da rabon abincin azumin na gwmanatin Kano, ya ce, tun bayan fara shirin a shekarar 2015, a duk shekara gwamnatin Kano tana kara adadain cibiyoyin rabon abincin don jama’a su amfana.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!