Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yaki da ‘yan bindiga: Gwamna Masari ya tura Karnuka gadin makarantun kwana a Katsina

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta amince da fara amfani da karnuka don kula da makarantun kwana da ke fadin jihar baki daya.

Kwamishinan ilimi na jihar Dr. Badamasi Chiranchi ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a garin Katsina.

Ya ce, karnukan za su rika tallafawa jami’an tsaro da ke kula da tsaron makarantun kwana ne da ke jihar.

A cewar kwamishinan an bai wa gwamnatin jihar shawara ce kan daukar wannan mataki, saboda karnuka suna da nasibi da Allah ya yi musu da za su iya gano marar gaskiya tun daga nesa.

A watannin baya ne dai wasu ‘yan bindiga suka sace daliban makarantar sakandiren Kankara su 342 kafin daga bisani jami’an tsaro su samu nasarar ceto su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!