Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Abin da aka tattauna tsakanin Abdul’aziz Ganduje da Sanata Barau

Published

on

Ɗan Gwamnan Kano Umar Ganduje ya kai wa Sanatan Kano ta Arewa Barau Jibrin ziyara.

A ranar Asabar ne hotunan ziyarar suka karaɗe kafafen sada zumunta, inda aka riƙa muhawara a kai.

Sanata Barau Jibrin dai na cikin manyan jiga-jigan tsagin Sanata Malam Shekarau, waɗanda suka shata layi da Gwamna Ganduje.

Me yasa Abdulaziz ya ziyarci Sanata Barau?

Abdulaziz da Sanata Barau Jibrin

Freedom Radio ta tuntuɓi Alhaji Murtala Alasan Zainawa, Daraktan yaƙin neman zaɓen Sanatan wanda ya tabbatar da ziyarar.

Ya ce, “Abdul’aziz Ɗanmu ne kuma mutum ne mai mu’amala, ya zo wajen Sanata ne domin ya yi masa godiya, kan aikin ginin makarantar da ya bai wa mahaifiyarsa”.

Ya ci gaba da cewa “Sanata ya bai wa mahaifiyar Abdulaziz aikin ginin makaranta a garin Malam Madori, wanda ita kuma ta bai wa Abdul ɗin aiwatar da aikin”.

“Yanzu an kammala shi ya sa ya zo domin ya yi godiya da ƙara ƙarfafa zumunci a tsakani” a cewar Zainawa.

To ko wannan ziyarar na nufin Abdulaziz ya dawo tafiyar G7?

Zainawa ya ce, ba abin mamaki bane domin kaso mai yawa na jami’an Gwamnatin Kano suna tare da tsagin G7 a ɓoye, lokaci ne zai nuna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!