Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Adadin masu dauke da Corona ya kai 1728 a Najeriya

Published

on

Cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta ce a ranar Laraba an samu karin mutane 196 da suka kamu da cutar Covid-19 a sassan Najeriya.

Cikin sanawar da NCDC ta wallafa a shafinta na Twitter a daren Larabar nan ta ce an samu karin ne daga jihohin Lagos inda aka samu karin mutane 87 sai Kano da ta samu karin mutane 24, Gombe ta samu karin mutum 18 sai Kaduna da aka samu karin mutum 17.

Birnin tarayya Abuja an samu karin mutum 16 sai Katsina da aka samu karin mutum 10, Sokoto ta samu karin mutum 8 yayin da jihar Edo ta samu karin mutum 7.

Jihar Borno an samu karin mutum 6, sai jihar Yobe da aka samu mutum 1, jihar Ebonyi da Adamawa ma an samu karin mutum guda-guda.

Har ila yau, NCDC ta ce yanzu haka adadin wadanda suka kamu da cutar a Najeriya sun Kai 1728 yayin da 307 suka warke sarai.

Guda 51 kuma suka rasa ransu sanadiyyar cutar.

Karin labarai:

Covid19: Badaru ya bada umarnin rufe karin kananan hukumomi hudu

BUK zata fara gwajin masu dauke da cutar Corona

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!