Labarai
Adadin yan ta’adda da ke mika wuya Arewa maso Gabas ya ƙaru- Rundunar Soji

Rundunar sojin Najeriya, ta ce, adadin ‘yan ta’adda da abokan hulɗarsu da suka mika wuya ga dakarunta a yankin Arewa maso Gabas ya ƙaru da kashi 213 a cikin mako guda.
Rundunar ta ce hakan na faruwa ne sakamakon ci gaba da ayyukan soji na Operation Hadin Kai, da nufin rage ƙarfin ‘yan ta’addan da kuma katse hanyoyin samar musu da kayayyaki.
Jami’in yaɗa labarai na rundunar haɗin gwiwa ta rundunar a Arewa maso Gabas, Kyaftin Mohammed Goni, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
A wani ci gaban kuma, wasu manyan mambobin ƙungiyar ta’addancin guda biyu sun mika wuya ga sojoji tare da miƙa makamai da alburusai.
You must be logged in to post a comment Login