Labarai
Rundunar Operation Hadin Kai’ ta buƙaci mazauna yankin Arewa maso Gabas su kasance cikin shiri

Rundunar sojin kasar nan da ke gudanar da aikin ‘Operation Hadin Kai’ ta bukaci mazauna yankin Arewa maso Gabas su kasance cikin shiri da taka-tsantsan a lokacin da ake gudanar da bukukuwan sallar layya
Jami’in yada labarai na Hedikwatar Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa maso Gabas, Laftanar Kanal Sani Uba, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Litinin.
Sanarwar ta mika sakon taya murna ga daukacin al’ummar Musulmi gabanin bikin Sallah da ake shirin gudanarwa ranar Laraba, 28 ga Mayu, 2026.
Rundunar ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin samar da ingantaccen tsaro tun kafin fara bukukuwan, domin tabbatar da yanayi mai cike da zaman lafiya da tsaro ga kowa.
You must be logged in to post a comment Login