Labarai
Adeleke ya sake lashe zaben Gwamnan Jihar Osun

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya sake lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar, bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya, INEC, ta bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara.
Adeleke ya samu kuri’u 511,067, inda ya lashe kananan hukumomi 19 daga cikin 30 na jihar. Dan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, ya zo na biyu da kuri’u 444,815, bayan ya lashe kananan hukumomi 9.
Jami’in da ya bayyana sakamakon, Mataimakin Shugaban Jami’ar Federal University Oye-Ekiti, Farfesa Joshua Ogunwole, ya ce Adeleke ya cika sharuddan doka, don haka ya ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben kuma ya dawo kan kujerar gwamnan jihar Osun.
You must be logged in to post a comment Login