Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

AFCON 2022: kasar Egypt ta kai wasan karshe bayan doke mai masaukin baki Cameroon

Published

on

Kasar Masar (Egypt) ta yi nasarar kaiwa wasan karshe a gasar cin kofin Afrika ta AFCON ta shekarar 2022 bayan doke masu masaukin baki kasar Cameroon.

Kamaru dai ta yi rashin nasara da ci 1 da 3 a bugun daga kai sai mai tsaran gida, bayan tinda fari an tashi wasa 0-0.

Fafatawar dai ta gudana a ranar Alhamis 03 ga Fabrairun 2022 a kasar ta Kamaru.

Kasar Kamaru dai itace ke karbar bakuncin gasar, sai dai rashin nasarar datai ya sa bazata lashe gasar ba.

Yayinda kasar Masar zatai yunkurin lashe gasar a karo na 8 a tarihi tin bayan fara gasar.

Wasan karshe dai zai gudana a ranar 06 ga watan da muke ciki tsakanin kasar Senegal wadda bata taba lashe gasar ba a tarihi.

Zuwa yanzu dai kasar Burkina Faso da kuma Kamaru za suyi wasan neman mataki na uku, bayan sunyi rashin nasara a wasannin kusa da karshe a gasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!