Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Akwai bukatar karin kungiyoyin tsaro a Kano

Published

on

Wata kungiya mai fafutukar tabbatar da tsaro mai suna Mafita ta bayyana cewa jami’an tsaron da kasar nan su kadai ba za su wadatar da kasar nan ba wajen magance matsalolin tsaron da ake fuskanta.

Shugaban kungiyar reshen Jihar Kano Kwamared Sani El- Mansur ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio, wanda ya tattaunawa kan harkokin da suka shafi tsaro a kasar nan.

Sani El-Mansur ya kara da cewa matsalar tsaro da aka samu ce ta sanya su kafa wannnan kungiya ta jami’an tsaron, don bayar da ta su gudunmawa ta hanyar tallafawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu.

LABARAI MASU ALAKA

Anyi kira ga shugaba Buhari da ya kawo karshen matsalar tsaro

Kano ba ta bukatar kafa rundunar tsaro -Ganduje

Rufe wajan hakar ma’adanai a jihar Kebbi zai taimaka wajan rashin tsaro

A na ta bangaren daya daga cikin jami’an kungiyar Malama Aisha Muhammad Jalo da ta kasance cikin shirin, ta bayyana cewar yanzu haka banagaren mata na kungiyar ya sanya idanu a kan yadda yaya mata ke fuskantar matsalar shaye-shaye, inda kungiyar ke kokarin ganin an samu sauki ta a bangaren.

Bakin sun kuma bukaci al’ummar gari da su kasance masu sanya idanu a kan jama’ar da ke shige da fice a Unguwanninsu, tare da kai rahoton duk wanda ba su aminta da shi ba, don ganin an samar da tsaro a tsakanin al’ummar kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!