Connect with us

Labaran Kano

Akwai yiwuwar Ganduje zai yi takarar Sanatan Kano ta Arewa

Published

on

Alamu na nuni da cewa Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje zai nemi takarar Sanatan Kano ta Arewa.

A wani saƙo da mai taimakawa Gwamnan kan kafafen sada zumunta Abubakar Aminu Ibrahim ya tabbatar da hakan.

Ya ce “Al’ummar ƙaramar hukumar Dawakin Tofa sun bai wa ɗansu Gwamna Ganduje gudunmawar kuɗi tare da magiya gare shi don ya fito ya wakilci Kano ta Arewa a majalisar dattawa”.

Jam’iyyar APC ce ke riƙe da kujerar sanatan Kano ta Arewa wadda Barau Jibrin ke kai, to amma baya tare da ɓangaren Gwamna Ganduje a jam’iyyar ta APC.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!