Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Akwai yiwuwar hana ‘yan wasan da ba a yiwa rigakafin Corona ba buga Kofin Duniya

Published

on

Mahukuntan kasar Qatar na ci gaba da duba yiwuwar saka yin ragakafin Corona ya zama tilas ga ‘yan wasan da za su halarci kasar don buga gasar cin Kofin Duniya na 2022.

A wani rahoto da Jaridar The Athletic ta Ruwaito , ya tabbatar da cewar kasar ba za ta bar dukkan wani dan wasa shiga kasar ba matukar ba ayi masa Rigakafin ba.

Manyan kungiyoyin wasanni su rinka tallafawa kanana-Sarkin Kano

Sai dai idan hukuncin ya tabbata, hakan ka iya kawo rudani tare da rasa wasu zakakurarrun ‘yan wasa da za su halarci gasar , kasancewar wasu da dama basu yarda da ayi musu Allurar Rigakafin ba.

A baya baya nan dan wasan tawagar Arsenal Granit Xhaka , ya ki Amincewa da ayi masa Rigakafin , tare da mai tsaron gida na Newcastle United Karl Darlow , duk da fama da cutar Corona da ya yi jinya da ita shi Darlow.

Kasar ta Qatar na shirin fara gwada yin Rigakafin ga ‘yan wasan da za su fafata a gasar Kofin Larabawa na Arab Cup, da za’a Fara a ranar 30 ga watan Nuwamba na 2021.

Samun nasarar shirin a gasar ta kofin na Larabawan , shi zai bada dama ga kasar ta Qatar ta aiwatar da manufar ta ga ‘yan Wasa, ‘yan kallo da jami’an da za su halarci gasar ko kuma akasin haka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!