Connect with us

Labarai

Amnesty International ta ƙaddamar da binciken gano masu ɗaukar nauyin faɗan daba a Kano

Published

on

Kungiyar kare haƙƙin bilʼadama ta Amnesty International ta ƙaddamar da bincike don gano ƴan siyasa da ke daukar nauyin faɗace-faɗacen daba a Kano.

Babban Daraktan Kungiyar a Najeriya Malam Isah Sanusi, ya bayyana hakan a tattaunawarsa da kafar Arewa Updates.

Ya ce, tuni suka ƙaddamar da bincike a kan yawaitar faɗace-faɗacen daban da ke da alaƙa da ƴan siyasa.

Ya ƙara da cewa, da zarar sun kammala bincike za su kwarmata rahoton sunayen ƴan siyasar da aka gano suna da hannu wajen ɗaukar nauyin ayyukan dabar.

Amnesty ta kuma yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta ɗauki tsattsauran mataki domin yawaitar faɗan dabar zai iya firgita mutane da hana su shiga harkokin zaɓe balle su samu damar kaɗa ƙuriʼa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!