Labarai
Gwamnatin Kano ta musanta kashe mutane 5 yayin rantsar da mataimakin Gwamna

Gwamnatin jihar Kano ta musanta kisan mutane biyar a jihar yayin rantsar da mataimakin Gwamna a ranar Talatar nan.
Hakan na dauke ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labaran Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar.
Sanarwar tace binciken da gwamnati da jami’an tsaro suka gudanar bai tabbatar da faruwar lamarin ba, sakamakon gaza samun rahoto a hukumance.
Sanarwar ta bayyana cewa rikicin da ake zargin wasu ‘yan daba sun yi, bai faru a kusa da gidan gwamnati ba, saboda haka bai kamata a danganta shi da bikin gwamnatin jihar ba.
Gwamnatin ta kuma nuna takaicinta kan yadda kungiyar Amnesty International ta wallafa rahoton ba tare da tantancewa daga jami’an tsaro ko hukumomin gwamnati ba, inda ta zargi kungiyar da dogara da bidiyoyin da ke yawo a kafafen sada zumunta.
You must be logged in to post a comment Login