Connect with us

Ƙetare

Amurka da Iran na iya sake komawa kan teburin tattaunawar sulhu

Published

on

Ana hasashen cewa Amurka da Iran na iya sake komawa kan teburin tattaunawar sulhu cikin ‘yan kwanaki masu zuwa.

 

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da jaridar New York Post, inda ya ce akwai yiwuwar samun wani ci gaba nan da kwanaki biyu, tare da nuna cewa Pakistan na daga cikin wuraren da ake dubawa domin gudanar da tattaunawar.

 

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da bangarorin biyu suka yi a karshen makon da ya gabata a Pakistan. 

 

A lokacin, mataimakin shugaban Amurka, JD Vance ne ya wakilci kasar, yayin da shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, da wasu jami’an kasar suka jagoranci tawagar Iran.

 

To sai dai, duk da tattaunawar da aka yi, ba a cimma wata yarjejeniya ba a tsakanin bangarorin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!