Connect with us

Labarai

Kotun koli ta sanya 22 ga watan Afrilu domin shari’ar ADC

Published

on

Kotun kolin kasar nan ta sanya ranar 22 ga watan Afrilun da muke ciki domin sauraron karar da shugaban jam’iyyar ADC na kasa, David Mark, ya shigar gabanta dangane da rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar.

 

Karar na da alaka da shari’ar da wani tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa, Nafiu Bala, ya gabatar, wadda ta haifar da takaddama a tsakanin bangarorin biyu.

 

Ana sa ran sauraron shari’ar zai ba da haske kan wanda ke da hurumin shugabantar jam’iyyar, yayin da rikicin ke ci gaba da jan hankali a fagen siyasar kasar.

 

Hukuncin da kotun za ta yanke na iya zama mai tasiri sosai ga makomar jam’iyyar ADC da kuma tsare-tsarenta a nan gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!