Labarai
Amurka ta kama mutane 10 ‘yan Najeriya da aikata laifuka

Hukumar Shige da Fice ta Amurka, ICE, ta fitar da sabbin sunayen ƴan Najeriya 10 da take shirin kora daga ƙasar bisa zargin aikata laifuka.
An wallafa sunayen mutanen ne a shafin ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurka, DHS, mai taken “Worst of the Worst”, wato “mafi muni cikin masu laifi”.
Laifukan da aka lissafa sun haɗa da zamba da satar bayanai, laifukan da suka shafi cin zarafinn yara, laifukan miyagun ƙwayoyi da kuma mallakar makamai.
Bayanan da aka wallafa a shafin na DHS, an bayyana su a matsayin baƙin haure da ICE ta kama bisa laifukan da ake zarginsu.
Ma’aikatar ta ce ƙarƙashin jagorancin DHS, jami’an ma’aikatar da ICE suna aiwatar da alƙawarin Shugaba Donald Trump na korar ɗimbin baƙin haure daga Amurka, inda suka fara da waɗanda ta bayyana a matsayin masu aikata manyan laifuka.
You must be logged in to post a comment Login