Labarai
‘Yan sanda sun kama wasu likitoci masu safarar Koda

Rundunar ’yan sandan kasar nan ta gabatar da wasu mutane huɗu, ciki har da likitocin ƙoda biyu, bisa zargin hannu a wata ƙungiyar safarar mutane da cire ƙoda ba bisa ƙa’ida ba a jihar Nasarawa.
Mai magana da yawun rundunar, CSP Ani Iniedu, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a. Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a ranar 19 ga watan Agustan 2026 a Auta Balifi, ƙaramar hukumar Karu ta jihar Nasarawa.
Rundunar ta ce ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin ya amsa cewa an yaudari wasu matasa masu fama da matsalar kuɗi, inda aka kai su asibiti aka cire musu ƙoda, tare da amfani da takardun bogi wajen gudanar da ayyukan. Bincike na ci gaba domin kamo sauran waɗanda ake zargin suna
You must be logged in to post a comment Login