Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An ɗage ranar komawa karatu a jami’o’in Nijar

Published

on

Ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jamhuriyyar Nijar ta ɗage ranar komawa karatu a jami’o’in ƙasa daga 1 ga watan Satumba mai kamawa zuwa 13 ga watan.

Rahotanni sun ce, ƙungiyar malaman jami’o’in ƙasar ce ta nemi Gwamnati ta ƙara wa’adin hutun, domin malamai su ƙara kimtsawa.

Freedom Radio ta tuntuɓi sakataren ƙungiyar malaman jami’o’i reshen jihar Tahoua Malam Namaiwa Atto Muhammadu ya ce, malamai basu gama shirin komawa ba, saboda sun yi ayyuka da yawa kafin hutu.

Namaiwa ya ce, Malaman sun yi aikin jarrabawar neman ƙwarewa ɗalibai da aka yi a makon da ya gabata, alhali suna cikin hutu, don haka suka nemi ƙari domin cike gurbin lokacinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!