Connect with us

Labarai

An fara sayar da hannun jarin kamfanin Mai na Dangote

Published

on

An buɗe hannun jari mafi girma a Afirka ga jama’ar da ke da sha’awar siyan hannun jari a matatar mai ta Dangote.

Matatar ta Ɗangote tana tayin sama da hannun jari biliyan huɗu a ƙarƙashin wata yarjejeniya da ake sa ran za ta samar da kusan dala biliyan 1.6.

Matatar ta ƙara da cewa tana son bai wa jama’a damar kasancewa masu hannun jari a matatarsa da ta soma aiki shekaru biyu da suka gabata kuma tuni ta kasance matata mafi girma a nahiyar Afirka.

Dangote ya bayyana cewa yana shirye-shiryen faɗaɗa aiki a matatar da za a kashe dala biliyan 14 wanda zai ruɓanya ayyukan matatar nan da shekarar 2029.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da farashin fetur ya kusa kaiwa naira dubu daya da dari hudu kan kowace lita zuwa ƙarshen watan Agusta a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!