Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

An gano Jakadiyan Tona Asiri

Published

on

An gano Jakadiyan Tona Asiri

Cikin wani sautin muryar tattaunawar waya ta juramin fina-finan Hausa Isa A. Isa ya bayyana cewa jarumar nan da ta yi fice a shafukan sada zumunta wato Sadiya Haruna ta san wanene Jakadiyyan Tona Asiri kuma suna da alaka da ita.

Saurari tattaunawar ta Isa.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/10/Isa-Jakadiya_audio.mp3?_=1

Jakadiyyan Tona Asiri dai wani asusu (account) ne da ya jima a dandalin sada zumunta na Instagram wanda yake wallafa bayanan Gulma da Tsegumi musamman a masana’antar Kannywood, al’umma da dama dai na son ganin shin ko wacece ko waye wannan Jakadiya?

Tunda farko dai wani rikici ne ya barke a tsakanin Isan da kuma Sadiyar inda kowa ke kokarin tona asirin dan uwansa.

Ita ma a nata bangaren cikin wani sakon murya da ta aikewa Jakadiyar Tona Asiri, Sadiyar ta yi maganganu da suke gab da gasgata maganar Isan.

Saurari jawabin Sadiya.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/10/Sadiya-Jakadiya_audio.mp3?_=2

Izuwa yanzu dai tuni wannan batu ya fara daukar hazo a shafukan sada zumunta inda jama’a suke ta bayyana ra’ayoyi mabam-bamta akai.

Allah ya kyauta.

Rubutu mai alaka:

An fara sulhu tsakanin jaruman da suka yi auren mutu’a

An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne

Kun san abinda ya hana jaruma Maryam Yahya aure?

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!