Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne

Published

on

Wani mutum mai suna Ibrahim Muhammad Jidda mazaunin garin Maiduguri ya bayyana cewa bidiyon nan da ake yadawa kan cewa Sheikh Aminu Daurawa ne ke tikar rawa a wurin taron biki ba gaskiya bane.

A cewar Ibrahim Muhammad Jidda cikin wani faifan sauti da ya saki a shafukan sada zumunta, a ala-hakika ba shi bane domin kuwa lamarin ya faru ne akan idon sa a wani dakin taro mai suna White Arena dake GRA a Maidugurin.

‘Yace mutumin da aka nuno a cikin bidiyon kani ne ga wani dan siyasa a Maiduguri da ya samu halartar bikin, amma sam ba Mallam Daurawa bane sai dai sunyi kama sosai da Mallam Daurawa din.

Saurari cikakken bayanin nasa a kasa:

https://www.sharfadi.com/wp-content/uploads/2019/10/An-gano-Wanda-yayi-rawa-a-bidiyon-da-wasu-ke-jinginawa-Sheikh-Daurawa.mp3?_=1

Tun da farko dai an fara yada wannan bidiyo ne wanda ke nuna wani mutum da wata suna tikar rawa a wurin taron biki inda aka rika yada shi da sunan cewa wai Mallam Daurawa ne ke waccen rawar.

Kalli wasu bayanai da aka wallafa a shafin facebook kan bidiyon a kasa.


Sai dai tuni Shehin malamin ya fito ya karyata labarin.

Rubutu masu alaka:

An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne

Za’a sanyawa unguwannin ‘yan gayu na’ura mai amfani da hasken rana

Buhari yayi ganawar sirri da Jonathan

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!